|
TAKAITACCEN TARIHIN KABIRU USMAN FAGGE
|
An haifi Kabiru Usman Fagge ne a kano, kamar shekaru sittin da suka gabata,
wato ran 12 ga watan Satumban shekarar 1946.
A shekarar 1956 ya shiga makarantar Firamare ta Fagge a kano, kuma a shekarar
1969 ya kamala karatun midil a Kuka Siniya, sannan ya wuce zuwa Kolejin
Horas da Malamai ta Bichi inda ya shekara uku sannan ya kammala a Kolejin
horas da malamai ta Kano, KTC a shekarar 1970, ya sami akardar shaidar
koyarwa mai daraja ta biyu (Grade2).
Daga shekarar 1971-74 ya koyar a makarantar Firamare ta Tudun wadar birnin
Kano, sannan ya koma karo karatu a Jami'ar Bayero, lokacin tana KarKashin
(ABU). Bayan ya sami Digirinsa na farko a fannin Musulunci da tarihi,
sai ya kama aiki a kamfanin wallafa Jaridun New Nigeria da Gaskiya Ta
fi Kwabo.
Kabiru Usman Fagge, na daga cikin ma'aikatan farko da marigayi Audu Bako
ya gayyato domin
bude gidan Telbijin na Kano-Bompoi a shekarar 1976. A shekarar 1986 NTA-Kano
ta bada aronsa domin ayyukan wayar da kan Alhazai a hukumar Alhazan Nigeria
(NPB) dake Ikko. sannan a shekarar 1989, Kabiru Usman Fagge ya kama aiki
a gidan Rediyon Muryar murka(VOA) inda har yanzu yake aiki. Kabiru Usman
fagge nada aure da 'ya'ya bakwai. Za'a iya aikawa Kabiru Usman Fagge da
wasiia ta afagge@voahausa.com
|
|