Hausa Hausa English
Wakokin Hausa

Chat Room
Check your mai

Classified Ad

Jaridu


Mahada

 

 

 

 

Bayani Kan Bakandamiyar Shata  



  Mutane da yawa suna jin dadin kade-kade da wake-wake, amma saboda hada addini da al'ada sai hakan ya zaina bidi'a ta fuskar addinin Musulunci. Kida da waka na iya zama bidi'a muddin maza da mata zasu hadu don su saurara. Yawaita habaici da mawakan Hausawa keyi da wasu yaren ma kan haddasa fitina a tsakanin mutane. Haka kuma mawaka kan daukaka mutumin da sukewa waka har yaji kamar ya fi kowa a duniya, bayan kuwa sanin Musulmi ne cewa babu wanda yafi wani a wurin Allah subhanahu wa ta'ala im banda wanda ya fi tsoron Allah.
Haka al'amura suka rika tafiya har zuwa bayyanar Mujaddadi Shaihu Usmanu Dan Fodiyo (Allah ya kara masa yarda) wanda a lokacinsa ya yi hani ga yin wakoki da kade-kade. Duk da haka mujaddadi Usmanu Dan Fodiyo bai hana yin wakar baka da wakar zube ba. Shi da kansa ya rubuta wasu wakokm kamar yadda dansa Muhammadu Bello ya rubuta kuma ya bayyana cikin (Inf'aq al-Maisur). Hana yin wakoki da kida ta sigar bidi'a da mujaddadi Usmanu Dan Fodiyo yayi ya karya zuciyar Hausawan dake sha'awar waka da kida, koda ki cikin fulatanci ne. Gefe guda kuma Maguzawa wadanda ba Musulmi ba a wai lokaci musamman a kasashen Hausa cikin Nijeriya, Niger da Ghana, Kamar Saliyo, an sami wadanda suka fara yunkurowa a filin kida da waka, kuma ba hadu da irin wancan hanin da aka yi masu ba. A dalilin haka za'a ga Hausaw kasashen Ghana da Niger sun kere na Nigeriya a filin waka da kida. Bayan akasarin kasashen Africa sun sami 'yancin kansu daga 'yan mulkin mallaka sami wani tashin gwauron zabin da mawaka da makadan hausa suka yi, yari kuma cikin wannan yunkurin ake yi na yin gasa da sauran kabilun Nijeriya filin waka da kida kuma ba za'a taba mantawa da yunkurin farko da mariga; irin Narambada, Musa dabalo, Inu Chaji, Mamman Sarkin taushi, Hamisu ft ganga, Mu'azu Dan alalo suka yi ba, A yanzu kuma ana damawa da Alh. Mu, dan kwairo, Sa'idu Faru a fannin kotso, su Alhaji Mamman shata Katsina a kida da wakar kalangu, kuma liar yau tare da Alh. Mamman shata ake dam; shi da kansa ya fadi haka cikin wadannan baitocin nasa a wakar Bakandarr indayake cewa:

Mutane kowa yake addini
kun sanbaya kamar Manzon Allah.
Kowa ka gani na sabon Allah,
ko wanene ke kafirci
kun san babu kamar Fir'auna.
To, ashe haka duk wanda ke yin waka, yara bai yi kamar Shata ba.

A duk lokacin da Alhaji Mamman Shata ya zuga kansa a wakarsa ta Bakandamiya sai ya bada dalili, kuma ya nemi duk wanda bai amince da hj ba yana iya fitowa filin waka a gwada a gani kamar yadda yake cewa cikin wannan baitin kamar haka:

Idan kuma kayi musu sanya
Mu gani ko daga ina a yi wakar.

Alhaji Mamman Shata Katsina ya nuna tausayinsa ga marokan birni da n; kauye masu yin kida da waka domin su sami na abinci, idan kuma kidan y; masu kyau suyi auren zamani. Babu shakka Bakandamiyyar Shata kalu-bale-ce ga duka maroka da makadan hausa. Yanzu kuma bari mu leka muga abinda wakar Mai martaba Sarkin Zazzau Dr. Alhaji Shaihu Idris ta kunsa.
 

Littatafan Hausa

 
Gidajen Rediyo Hausa

 

 

       
 

Mohammed Hashim Gumel ya tsara ya gina wannan shafi. Kofar mu a bude take bisa duk wasu shawarwari da kuma ra'ayoyinku, kan wannan fili, da kuma irin abinda kuke so mu rika wallafawa."Gyara kayanka bai zama sauke muraba ba." Ana iya aiko mana da wasika ta layi kamar haka mhashim@gumel.com

@Gumel.com 1998 Wannan fili an kareshi da dokar wallafawa, a nemi izzini kafin amfani da kayan mu.