Hausa Hausa English
Wakokin Hausa

Chat Room
Check your mai

Classified Ad

Jaridu


Mahada

 

 

 

 

Hikimar Dake Akwai Cikin Wakokin Shata 


 
Akwai wakoki da yawa wadanda Alhaji Marnman Shata yayi don kansa ba are da an bashi kudi ba. Akwai na kishin kasa kamar wadda yayi ta 'yan arewa ku bar barci Nigeriar mu akwai dadi. Akwai ta kowa ya shiga dajin rugu da wadda ya yiwa kogin Bahar Maliya da wakar gargajiya da kuma wadda ya nuna lankwasa harshen Hausa a wakarsa ta " ayaure duniya labari". Yana daya daga cikin tsarin hikimarsa ta waka wajen jeranta kalangu da wakarsa wanda hakan ke taimaka masa ganewa a duk lokacin da makadinsa ya dan yi kuskure sai ya gyara ta hanyar kwalmada wakar da zata dace da kidan don hana mai saurare gane kuskuren da wuri. Idan kuma aka dubi wakar dajin rugu za'a ga yadda Alhaji Mamman Shata ke kamanta halayyar zaman duniya da ta namun daji. Akawi kuma wakar nomadonjan hankali jama'a su koma ga aikin noma don cida kansu da kasa baki daya.

Cikin wakarsa ta 'yan Arewa ku bar barci, hikimar da ya nuna a wakar tasa mafi yawa daga cikin mutanen Arewa suka fara ajiye kudinsu a Bankuna. Hikimar dake tattare cikin wakokin Alhaji Mamman Shata sai an natsu sosai za'a zakulo su saboda lankwasar da yake yiwa luggar Hausa don ta dace da zamanin da ake ciki. Yana kuma amfani da kalmomin Hausa masu saukin fahimta. Idan aka dubi tsarin wakokin Alhaji Mamman Shata wadanda suka kusanci jinin sarauta, za'a ga ba kamar sauran makada da mawakan Fada bane domin Alhaji Mamman Shata bai ta'allaka kan wani Sarki guda kamar yadda marigayi Narambada makadin Sarkin Gobir Isa da sarkin taushin Sarkin Katsina da Jankidi, makadin Sarkin Musulmi da Marigayi Abdul-Rahaman sarkin kotson Sarkin Kano wanda shima ya gaji marigayi Alhaji Musa Dabalo. Alhaji Mamman Shata, kamar yadda yake cewa ne cikin wakarsa ta Bakandamiya:

Fadawa mutane na kowa
ya rasa Shata yayi asarar waka,
ko wanene kuma ko dan wa.

Wannan ya nuna ke nan Alhaji Mamman Shata mawakin Hausa ne na kowa da kowa duk da cewa bai gaji kida da waka ba idan aka dubi jerin wakokinsa za'a ga ya dara wadanda suka gaji kida da waka. A lokaci guda idan ta raya masa ko aka shaida masa abinda zai yiwa waka sai kawai ya fara kuma mai kalangu da 'yam amshinsa su tafi tare kamar yadda ake bukata.

Alhaji Mamman Shata bai bar ma'aikatan Gwamnati a baya ba domin ya yiwa Alhaji Sa'idu Barda da Abdu V.I.O. wakoki, ga kuma wakar da ya yiwa Mamman da da wadda ya yiwa marigayi Kanal Abba Siri-Siri da marigayi Sani Audi Katsina. A Bangaren attajirai banda wakokin da aka tsara a wannan littafi, akwai wadda kuma ya yiwa marigayi Alhaji Haruna Kassim Ringim wanda shi ya fara kai Alhaji Mamman Shata aikin Hajji. Ana iya samun tabbacin haka cikin wadannan baitocin dake cewa:

Rannan na da wo daga tashe birni
sai Haru yace kai makadi aje
'yarganganrka, kazo na kaika
ka gano dakin Allah.

Sauran attajiran da Alhaji Mamman Shata ya yiwa waka sun hada da Alhaji Ali Kotoko da Alhaji Bukar Mandara dukkansu dake zaune a jihar Barnon Nijeriya. Babu shakka idan aka dubi tsarin wakokin da Alhaji Mamman Shata yayi da wadanda sauran mawakan fada suke yi, za;a gane cewa wakokin Alhaji Mamman Shata sun zama sune a gaba kuma wadanda keda saukin samu a kowane lokaci.Gwamnatin mulkin soja karkashin jagorancin janar Olusegun Obasanjo mai ritaya ta baiwa Alhaji Mamman Shata lambar girma cikin shekara ta 1976. Jamrar Ahmadu Bello ta Zariya ita ma ta bashi lambar girma shi yasa ake yi masa lakani da Dokta Mamman Shata Katsina.
Dangantaka tsakanin Alhaji Mamman Shata da sauran mawaka a wani gefen tana da danko amma mafi yawa saboda hassada mawakan Hausa basa kaunarsa. Dalili ke nan a wakarsa ta Bakandamiya yake cewa:

Goge da Molo wargin yara ne
su sami abinci suyi shakwara suyi jamfa,
idan sun sami kudi suyi auren zamani.

Daga cikin mawakan Hausa, marigayi Alhaji dan Anace yafi yin farat-farat da Alhaji Mamman Shata duk da cewa shima ya sami kishiya a filin wakar Dambe. Alhaji Mammman Shata baya barin sai ta kwana. idan anyi masa abu nan da nan yake kokarin ramawa ko ya bayyana ra'ayinsa na kin abin. Alal misali idan aka dubi bayanin da ya yi a lokacin da Sarauniyar Ingila ta ziyarci Nijeriya a zamanin marigayi Alhaji Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Allah ya jikansa. An gayyato A'ishat Fallatiyya daga Sudan don yin waka, ganin haka sai Alhaji Mamman Shata ya rera wakar dake nuna kishi inda yake cewa:

A gaya maka Ahmadu jikan Shehu
taura biyu bata tauno koda kuwa,
a bakin kura ne.

 

 

Littatafan Hausa

 
Gidajen Rediyo Hausa

 

 

       
 

Mohammed Hashim Gumel ya tsara ya gina wannan shafi. Kofar mu a bude take bisa duk wasu shawarwari da kuma ra'ayoyinku, kan wannan fili, da kuma irin abinda kuke so mu rika wallafawa."Gyara kayanka bai zama sauke muraba ba." Ana iya aiko mana da wasika ta layi kamar haka mhashim@gumel.com

@Gumel.com 1998 Wannan fili an kareshi da dokar wallafawa, a nemi izzini kafin amfani da kayan mu.