Hausa Hausa English
Wakokin Hausa

Chat Room
Check your mai

Classified Ad

Jaridu


Mahada

 

 

 

 

Yalwa Kanwar Shate 


  Alhaji Mamman shata ya fada da bakinsa cewar mahaiflnsa wanda bai ayyana sunansa ba yana da 'ya'ya uku. Biyu maza, mace guda. Sunan macen line Yalwa wadda kanwa ce ga Alhaji mamman shata, a dalilin haka ne yasa ke masa kirari da cewa shatan Yalwa kwana wasa. A lokacin da Alhaji [amman shata ke yaro ya saba da ya tashi da sassafe ya kora shanunsa zuwa iwo, wani lokaci tare da abokansa. Asalinsa bafulatani ne wanda iyayensa ika sanya shi a makarantar allo don ya koyi karatun Alkur'ani mai tsarki tun ana da shekaru biyar da haihuwa a duniya. Malam Ahmadu ne Malaminsa na irko. Bayan ya fara sanin baki sai ya koma wajen Malam Imamu dan Alhaji audu. Ya kuma yi karatu wajen Malam Ali. Alhaji Mamman shata yace babu Dinda yaki jini a lokacin da yake makarantar allo kamar kururuwar 'yan akaranta da ake kira kolaye musamman cikin dare lokacin da 'yan ci rani kan ira wuta domin yin tilawa ko kuma a kiskadi.

Alhaji Mamman shata bai tsaya ya sauke Al-kur'ani ba ya fada sana'ar saida >ro. Amma kafrn ya bar makarantar allo saida ya sami na tsarki da salla. Bai u bada cikakken bayanin dalilin da yasa ya tsere daga makarantar allo ba. akar Asauwara ce wakar da take tashe cikin 1936 lokacin da Alhaji Mamman tata ya fara kwankwasa kofar film waka. Ga abinda yake cewa cikin wakarsa
Bakandamiya:
irarin waka bai san tsoro ba na fito shata ne, ya san ku, in san shi, sai kaka?
Malam Ya'u babban yaron Alhaji Mamman shata ya tabbatar da cewa ita wannan waka ta Asauwara Shata ne ya fara amma ba'a samu a gutsurata cikin wannan littafin ba saboda rashin sanin tabbacin wanda ya kirkirota. Amma ance masana tarihin al'adun hausawa yanzu sun dukufa wajen samo ainihin tarihin wannan waka. A kashi na biyu na wannan littafi za'a bayyana sakamakon

binciken masana tarihi kan wakar Asauwara. uaga cik.ui da Alhaji Mamman shata ya fara zama akwai Malunfashi da Bakori. Daga Bakori ne ya wuce zuwa Kano. Bayan ya dan shakata a Kano sai ya koma gida Musawa dake jihar Katsina ta yanzu. Da ya sake fitowa a karo na biyu sai ya yada zango a Funtuwa, sannan ya zarce zuwa Kano. A kasashen waje kuwa, Alhaji Mamman shata ya ziyarci Abija ta kasar Ivory Coast, ya kuma je Makka1 inda ya sauke farali na aikin Hajji. Alhaji Mamman shata bai manta da yawon duniyar da yayi na kasashen yammacin Africa ba domin ya bayyana duk wuraren da yaje cikin wakarsa ta duniya mafarki ne Alhaji Shata.

 

Littatafan Hausa

 
Gidajen Rediyo Hausa

 

 

       
 

Mohammed Hashim Gumel ya tsara ya gina wannan shafi. Kofar mu a bude take bisa duk wasu shawarwari da kuma ra'ayoyinku, kan wannan fili, da kuma irin abinda kuke so mu rika wallafawa."Gyara kayanka bai zama sauke muraba ba." Ana iya aiko mana da wasika ta layi kamar haka mhashim@gumel.com

@Gumel.com 1998 Wannan fili an kareshi da dokar wallafawa, a nemi izzini kafin amfani da kayan mu.