|
Tarihi ya nuna cewa Mangawa (Barebari) suka
kafa Garin Lautai, Wanda a zamanin yau ake kira Gumel. Kamar
yadda Masana tarishi suka bayyana cewa Mangawa (Barebari),
sun kauro ne daga kogin Maliya a kasar Masar, suka dinga yada
zango a gurare daban-daban har sai da suka sami yada wani
gagarumin zango a Ngazargamu, a kudancin Cadi. Wannan shine
babban yada zango da suka yi a shekara ta 1480, wanda shine
lokacin da aka kafa ta karkashin Shehun Borno, kamar yadda
aka santa a yau. Bayan karamin lokaci ba da jimawa ba, sai
wadannan bakin suka sake kwasar kayansu suka yi gaba. Wannan
karon shine kuma suka doshi yamma saida suka dangana da wata
fada mai suna Tumbi, suka huta sa’annan suka kara kutsawa
zuwa Gumel, inda suka kafa masaukinsu na karshe, tsakanin
1729-1848
|
|