|
Kabilar Hausa dai,kabilace dake
zaune a arewa maso yammacin taraiyyar Nijeriya da kudu maso
yammacin jamhuriyyar Nijar. Kabilace mai dimbin al'umma, amma
kuma a al'adance mai mutukar hadaka, akalla akwai sama da mutane
miliyan hamsin da harshen yake asali gare su. A tarihance kabilar
Hausawa na tattare a salasalar birane.Hausawa dai sun sami kafa
daularsu ne tun daga shekarun 1300's, sa'adda suka sami nasarori
da dauloli kamar su daular Mali, Songhai,Borno da kuma Fulani.
A wasu lokutan Hausawa sun sami gagarimin ikon, mulki da hadaka
ta kau da baki'yan neman ruwa da tsaki,da kuma neman angizon
a cikinta da kuma harkallar bayi. A farko-farkon shekaru na
1900's, a sa'adda kabilar Hausa ke yinkurin kawar da mulkin
angizo na fulani,sai turawan mulkin mallaka na Birtaniya suka
mamaye arewancin Nijeriya, da kuma kafa manufofin mulkin bayan
gida,a bisa karkashen mulkin birtaniya,'yan mulkin mallaka sai
suka marawa fulani baya na cigaba da manufofin angizon siyasarsu,
har yanzu dai mulkin kamin gambiza tsakanin Hausawa da Fulani
shi ne yayi kane-kane a arewacin Nijeriya. Wannan hadakar gamin
kambiza, an farota ne tun asali a matsayin fulani su dare madafun
ikon a tsararren tsarin siyasar arewa.Akasarin masu mulki na
fulani sun kasance yanzu, a al'adance hausawa gwamitse
Ko da yake, Hausawa na farko-farko maharba
ne, amma ya zuwan addinin islama da kuma karbansa da hannu
bibbiyu ya sanya labari ya sha bambam.Ginshikokin al'adun
hausawa na da mutukar zaranta, kwarewa da sanaiya fiye da
sauran al'ummar dake kewayenta. Sha'anin noma ita ce babbar
sana'ar hausawa inda hausawa ke ma sana'ar noma kirari da
cewa, na doke tsohon ciniki kowa yazo duniya kai yatarar,
akwai kuma wasu sana'o'in kamar su sha'anin jima watau harkar
fatu, rini, saka da kira, fannonin dake mutukar samun cigaba
a harkokin sana'o'in hausawa. Hausawa dai sun jima da shahara
wajen harkar fatauci kana kuma masu arziki na taka rawa a
sha'anin yau da kullum, tare da masu mulki da masana. Harshen
Hausa shi ne mafi girma da kuma mafi sanai'yar harshe a nahiyar
Afirka, harshen hausa ya aro wasu kalmomi daga wasu harsuna
musamman larabci kana kuma harshen na tafiya tare da yanayin
mu na zamani bisa al'adar cudeni-na cudeka. Harshen Hausa
dai ya zama harshen yau da kullum ga miliyoyin jama'a da ba
hausawa bane a nahiyar Afirka.
Bugu da kari, akwai cincirindon al'ummar Hausawa
a manyan biranen yammacin Afirka da arewacinta da kuma yankunan
cinikayyar al'ummar Hausawa da kuma yankunan da Hausawa suka
jima suna bi a hanyar ta zuwa aikin hajji. Akwai kuma rubutattun
adabi masu zurfi da kasidodi da kuma rubuce-rubuce a rubutun
ajami da aka buga tun kafin zuwan turawa yan' mulkin mallaka
na birtaniyya. Har ila yau, kuma wani tsarin rubutu a ajame
da aka kirkiro tun kafin zuwan turawa, da ba kasafai ake amfani
da shi ba yanzu.
|
|