Hausa Hausa English
Wakokin Hausa

Chat Room
Check your mai

Classified Ad

Jaridu


Mahada

 

 

 

 

Abin Da Mutum Ya Shuka Shi Zai Girba, In Hairan Hairan, In Sharran Sharran 


  Wata rana an yi wani mutum wanda ba shi da da, ba shi da jika. Ya yi maganin duniyan nan don ya sami da, Allah bai nufa ba, ya gaji ya dangana.

Ran nan yana zaune a kofar gidansa, sai ya ga wani ya kama dansa yana ta duka, ba ji ba gani, sai ya ce, “M, Allah mai girma! Dubi wani Allah ya ba shi har yana bugu, ni kuwa ga shi ina nema ruwa a jallo, Allah bai nufe ni da samu ba. In da ni Allah ya ba wannan, kome rashin jin kansa, me zai sa in buge shi? Da da ya yi jin kai, da kada ya yi, ai duk uwarsu daya, in ba dai don battan basirar mutane ba.”

A kwana a tashi, ran nan sai Allah ya ba matar mutumin nan ciki, bayan wata tara ta haifi da namiji. Aka yi suna, aka sa wa yaron nan Hafaru. Yaron ya girma a sangarce, kome ya yi uban ba ya ce masa kanzil. Ta kai dai fagen yaron nan ba ya jin kan uban, balle ya taimake shi. Don son da uban nan ke yi wa dan har abinci ma tare su ke ci, har ya kai ga aure ba su raba kwarya da ubansa ba.

Da ubansa ya fara tsufa sai Hafaru ya rika kyamar cin abinci da shi. In suna ci sai ya hana uban ya taba gabansa, yana cewa wai uban ya faye kazanta, duk yana barin majina a hanci, wai kuma ga shi da yawan tari, yanazuba musu yawu a ciki. Uban dai bai ce masa koma ba. Ana nan dai har ya kai ga fagen yana ci hannu na rawa, na baka na fadowa cikin kwarya. Sai dan ya buga masa tsawa ya janye kwanon abincin, ya ce sai ya ci kana ya ba uban.

Suna nan haka, sai ran nan Hafaru ya ce wai uban ba ya sude kwarya, kullum sai ya bar kwano cakal, duk ya bata shi da yawu. Saboda haka sai ya samar wau uban akushi, aka rika zuba masa nasa abincin dabam. Ran nan yana ci garin makyarkyata sai ya tuntsurad da dan akushin, tuwon ya zuba. Hafaru ya zo ya yi ta yi masa fada, wai ya faye gidi-gidi. Saboda haka sai ya tafi kasuwa ya sawo kwami irin na ban ruwan shanu, ya kawo gida ya rika zuba wa uban abinci a ciki, ya ce, “Ture wannan kuma, mu gani!”

Uban da bai ce kome ba, sai in abin ya dame shi ya yi ta kuka yana cewa, “Wannan dai duk laifina ne da na ki kwabonsa tun yana karami. Amma ba kome, Allah ya ba da mai rama mini.”

A kwana a tashi, sai ran nan Allah ya ba matar Hafaru ciki, ta haifi da namiji, aka sa masa suna Ishiye. Da ya kai shekara hudu ya yi wayo, sai ya zama ba shi da wajen wasa sai tare da kakansa, ko abinci ma tare su ke ci. Uban ya yi ya yi ya hana shi cin abinci da kakan, yaro ya ki. Saboda yaron nan har aka rika sa wa abincin tsohon mai da nama. Kome yaron nan ma ya samo sai ya nufo kakansa.

Ana nan har Ishiye ya kai shekara shida, ran nan suka tafi gona da uban, yana rike masa da goran ruwa. Da suka isa uban ya yi ta noma, har rana ta yi tsaka, sai ga matarsa, uwar yaron, ta kawo masa abinci, ya kakkabe hauyarsa, ya zo ya zauna yana ci, matar kuwa ta zauna kusa da shi. Sai yaron ya dauki wani dan guntun gatari da ke nan, ya shiga gona ya fara saran wata ‘yar itaciya da ke ciki, kwas, kwas, kwas. Da uban ya hanga ya gan shi, sai ya ce, “Kai me ka ke yi nan? Ajiye wannan abin banza, ka zo ka ci abinci. Haka ku ke yi har ku sare ‘yar kafarku, ku bar mutane da jiyya.”

Da yaron nan ya ji haka, sai ya ce wa uban, “Ci naka, ka bar mini nawa nan. Ni ina nan sai na sare itacen nan tukuna, ina so in gyara rassan ne in yi maka dan kwami da shi, in kai gida in ajiye, don in ka tsufa in rika zuba maka abinci a ciki!”

Da iyayen yaron nan suka ji haka, sai suka yi nadama, suka rike baki suka ce, “Ashe gaskiya ne abin da mutane ke fadi, kome ka shuka shi ka kan girba.”

Daga nan Hafaru bai sake iza keyar yaron nan har gida. Da isarsu gida Hafaru ka kama hannun dansa har wajen kakan. Ya durkusa, ya gaya wa tsohon abin da yaro ya ce a gona, ya kuma sake durkusawa ya roki tsohonsa gafara, yana ahi da kuka bisa ga abubuwan da ya yi masa. Yaro na kallo, bai san abin da a ke yi ba. Tsohon nan ya ce, “Mhm. Ai duk abin nan da aka yi, ni na ja. Je ka, na gafarta maka duniya da lahira.”

Hafaru ya tashi yana murna. Daga ran nan bai sake, tozarta ubansa ba, har Allah ya nufa ya cika a hannunsa, suka rabu da alheri. Kullum in Hafaru ya ga dan nan nasa, in ya tuna da maganar da ya yi, sai ya rike baki ya ce, “Ya’yan zamani, saninku baa sanin halinku ba!”

Da Musa ya ji aku ya kai karshen wannan labari, ya ce, “Wannan labari naka gargadi ne mai amfani ga wanda ya ji shi.”

Aku ya ce, “Ba wannan kadai ba, duk labarin da na ke bayarwa, in ka lura, ka ga haka ya ke. Ai ba muni ga mutum da ya fi ya kai muddin mutane bai iya bakinsa ba. Ga wani karamin misali nan na kunkuru da gauraki.

 

 

Koma Baya



{talla}

Littatafan Hausa

 
Gidajen Rediyo Hausa

 

 

       
 

Mohammed Hashim Gumel ya tsara ya gina wannan shafi. Kofar mu a bude take bisa duk wasu shawarwari da kuma ra'ayoyinku, kan wannan fili, da kuma irin abinda kuke so mu rika wallafawa."Gyara kayanka bai zama sauke muraba ba." Ana iya aiko mana da wasika ta layi kamar haka mhashim@gumel.com

@Gumel.com 1998 Wannan fili an kareshi da dokar wallafawa, a nemi izzini kafin amfani da kayan mu.