|
Wata rana wadansu samari su uku, abokan juna suka
tashi daga garinsu za su wani gari neman aure. Kowane ya yi
wankin kayansa, suka yi ado, suka kama hanya. Suna cikin tafiya,
sai karamin ya ce, “Ku ci gaba, na iske ku ni zan ratse.
Suka wuce, shi kuwa ya ratse, ya rabu da hanya kadan sai
ya tarad da wani dan akwati, barayi sun sato ya fadi. Ya duba
gabas, ya duba yamma, bai ga kowa ba, ya duka ya dauki akwatin,
ya ji da nauyi, ya nemo wani dutse ya fasa. Da hannun rigarsa
ya kunshe, ya fito da gudu ya bi ‘yan’uwansa yana kira. Da
suka ji kira, suka tsaya. Ya ce, “Albishirinku!”
Suka ce, “Goro.”
Ya ce, “Kun ga abin da na tsinta.” Kowane da ya kyalla ido
ya ga duki, duk suka yi ta murna, suka koma gefen hanya suka
kidaya, suka ga fam ashirin da hudu ne da sisi. Wanda ya tsinto
kudin na kirki ne, saboda haka ya ce, “Sai a raba, kowa ya
sami fam takwas takwas, sisin nan kuwa mu sayi abinci da shi
mu ci.”
Da babbansu ya ji haka sai ya ce, “To, madalla, mn gode,
Allah ya bar mu tare! Amma abin da ya fi, sai ka tafi gari
maza kudin, in ka dawo sa’an nan mu raba.”
Yaron da ya tsinci kudin ya tashi, ya nufi gari da gudu.
Da bacewarsa sai babban ya ce, “Abin da ya fi sai mu yi dabara
mu karbe kudin nan, mu raba mu biyu, watau fam goma sha biyu
biyu ke nan.”
Daya abokinsa ya ce, “Lalle gaskiyarka. To, yaya za mu yi
ke nan?”
Babban ya ce, “Ina da dabara. Ga wani maharbi can, mu kirawo
shi mu ce ya shiga kogon itacen nan, in an yi magana ya rika
amsawa.”
Suka kira maharbi, suka gaya masa duk abin da su ke so ya
yi musu, da abin da su ke so su karbe wa dan’uwansu, har suka
ce sa ba shi lada. Da maharbi ya ji batun kudi haka ya yarda.
Ya shiga kogon ke nan sai yaron ya komo. Da hango shi, sai
suka fara kuka. Ya ce, “Lafiya?”
Suka ce, “Ina fa lafiya, itacen nan ya kwace kudi duka!”
Yaron ya dubi itace, ya ce, “A’a karya ne, itace da ba ya
magana ma, ina ya kai ga sata? Ku dai ku sake shawara.”
Daga nan sai mutumin da ke cikin itace ya ce, “Wace shawara
za a sake? Ni na dauke. Kuma in kana tsammani kai ka fi ‘yan’uwanka
jaruntaka, to, zo karbi. Matsiyata ‘ya’yan zamani, wadanda
ko iyayensu ma ba su san girmansu ba, balle wani!”
Ko da yaro ya ji haka sai ya garzaya, bai zame ba sai gidan
Sarki. Ya gaya masa duk abin da ya faru tun daga farko har
karshe.
Sarki ya ce, “An tasam ma munafunci. Yaya za a ce itaciya
ta yi magana? Ina ‘yan’uwanka?”
Yaro ya ce, “Suna can gindin itaciya.”
Waziri ya dubi Sarki, ya ce, “Ranka ya dade, ai sai ka sa
ni in tafi in ji in gaskiya ne. Ka san ikon Allah ya fi da
haka.
Sarki ya ce, “To, sai ka tafi ka gani.”
Yaro ya shige gaba har gindin itaciyan nan, suka tarad da
‘yan’uwansa can suna ‘yan koke-koke kamar da gaske. Da ganin
Waziri suka ce, “Alhamdu lillahi!” Suka fadi suka yi gaisuwa.
Waziri ya dube su, ya ce, “Ku ne itaciya ta kwace muku kudi?”
Suka ce, “I, mu ne, ranka ya dade. Daga mun zauna nan gindinta
muna kidayawa, sai muka ga guguwa ta tashi ta murtuke wurin,
duk kura ta buce mu, muka rasa inda mu ke. Can an jima sai
ta natsa, muka duba kudin da ke gabammu, suka ce dauke mu.
Muka shiga tonon kasa, don muna tsammani kura ce ta rufe su,
ba mu ga ko kwabo ba. Muka tashi za mu yi fada da juna, don
ta kammu yayin da guguwa ta buce mu. Da muka fara zage-zage,
sai muka ji kamar daga sama an ce, “Kada ku zargi junanku,
ni na dauki kudin. In kuwa kuna jin wata-wata ne ku zo ku
kwata. Muka duba babu kowa, sai dai magana mu ke ji na fitowa
daga itaciyan nan.”
Da maharbin nan na cikin itace ya ji haka, sai ya nisa,
ya ce, “M, wannan dahir ne.”
Waziri ya dube su, ya ce, “A’a! Ai kuwa ashe da gaske ne.”
Itaciya ta ce, “Af, da kana tsammani karya ne” Sai ka zo
ka kwatam musu.”
Ko da Waziri ya ji haka sai ya rike baki, ya ce, “Ki yi
mini gafara, ni ba ruwana, aiko ni aka yi.”
Nan da nan sai ya aika aka fada wa Sarki ya zo da kansa
ya gani, domin a ce gani ya kori ji. Can an jima ya tinkaro
duk da mutanensa. Da isowarsa Waziri ya ce, “Ranka ya dade,
ka ga ‘yar itaciyar da a ke markabu kanta.”
Da maharbi ya ji haka sai ya ce, “Wai, wai, wai, ni ce ‘yar
itaciya! Kai ne wa tukun da ka ce mini ‘yar itaciya? Har dan
tsugunin nan naka ka isa zagina? Daga yau ba ka sake duban
kamata ka ce mata ‘yar itaciya ba!”
Da jin haka fa, sai hantar Waziri ta kada,ya fadi ya yi
sujada yana ta ahi, yana rokon gafara. Sarki ya tsaya tsayin
daka, ya dubi kogon itaciyan nan, ya ga lalle mutum na iya
shiga. Ya lura da gindinta kuma ya ga sawun mutum kamar ya
hau ta, ya dubi takon nan ya ga dai bai yi daidai da na ko
daya daga cikin samarin nan masu kudi ba. Ya tuna tun da ya
ke bai taba jin ma wanda ya ji maganar aljannu haka a fili
ba. Kai, karewa ma dai tun da Annabi ya kaura aka bar jin
irin wannan al’amari. Ko da ya lura da haka sai ya hakikance
makirici dai aka kulla, don a cuci yaron nan da ya tsinci
kudi. Sai ya dubi Waziri da ke ahi, ya ce, “Kai, tashi! Kwaure
ka ke wa sujada?” Ya juya wa itaciyar, ya ce, “Yanzu dai ko
ki ba su kudinsu tun da girma da arziki, ko kuwa in sa a kone
ki. Da mutum da aljani ni duk wanda ya tasam ma zalunci cikin
kasata sai na ga iyakarsa!”
Sai itaciyar ta ce, “Kai dai tsaya kan mutane. In ka fada
aljannu sai kai a ga iyakarka.”
Sarki ya dubi mutanen da ke nan, ya ce, “Duk ku saro kirare.”
Suka ruga nan da nan suka cika gidin itaciyan nan da itatuwa
da kirare.
Ya ce, “A kawo ashana.” Aka mika masa. Ya tasam ma itaciyar
zai kunna mata wuta, duk kowa ya rike baki. Maharbi ya ga
dai in ya kyale minti biuy, lalle zai halaka. Sai ya yi kara
ya ce, “Don Allah, ranka ya dade, kada ka sa wutan nan. Ni
ba kowa ba ne, mutum ne. Bari in sauko don Allah!”
Nan da nan sai mutum ya tsirgo daga kogo, da kudin rike
a hannunsa. Ya fadi ya gai da Sarki, ya tsunguna nan, ya fede
masa biri har wutsiya.
Sarki da mutanensa suka yi mamakin wannan al’amari. Mutane
suka ya ta cewa, “Lalle Sarki shi ma aljani ne.” Nan take
Sarki ya sa aka yi wa yaran nan biyu azzalumai, da maharbi,
bulala hamsin hamsin, ya sa aka kai su gidan kurkuku su yi
wata shida shida, ran da za su fito kuma a kewaya da su gari,
kowa ya gan su. Ya dauki kudin duka ya ba yaron abinsa. Yaro
ya fadi ya yi gaisuwa, ya tashi ya koma gidansu. Sarki kuma
ya koma gida. Kullum I an ta da tadi, in ya dubi Waziri, ya
tuna da yadda ya yi goho da katon bujensa, sai ya yi ta dariya.
Musa ya yi murmushi ya ce, “Ai ba Sarkin nan kadai ba, kowa
ya ji wannan labari ya yi dariya. Munafunci dai ba shi da
amfani.”
Aku ya ce, “Ina ka san munafunci ba shi da amfani, tun da
ba ka ji labarin Kado ba, da wadansu ‘yam fashi guda uku?”
Musa ya ce, “Har ya fi wannan dadi? Ban yi tsammani ba.
To, yaya suka yi? Fada mini mu ji.”
Aku ya ce, “Wannan din me? Kasa kunne ka ji.”
|
|