|
Domin wai akwai wani masassaki a Katako, yana
da ‘yarsa mai shekara biyar da haihuwa, sunanta Halima. Ko da
ya ke an san yaro a kan son tambayar kome ya ji ko ya gani,
duk da haka son tambaye-tambayen Halima sun wuce kima.
Wata rana da safe uban na zaune na sasakar wata kujera sai
Halima ta shigo, ta ce masa “Baba, inna ta ga mussa ta ce
mata kyanwa, ashe ba ta san sunanta ba, ko ta sani ke nan?”
Kafin uban ya bayyana mata da mussa a kyanwa duk daya ne,
sai ta sake masa wata tambaya, ta ce, “Baba, kawu ya ce wai
akwai giwa na yawo nan sama, ita ce ke yin fitsari da damina
muna cewa ruwan sama, gaskiya ne?
Uban ya fashe da dariya, zai bayyana mata ba gaskiya ba
ne, sai ta ce, “Baba, wai kai ma inna ce ta haife ka?”
Uban ya ga za ta hana shi aiki da surutu, sai ya ce mata,
“Fita waje can ki yi wasa da yara, sai in na kare ki dawo.”
Sai ta tashi ta ruga. Tana fita, sai ta ji yara na bin wani
wada, suna cewa, “Malam Dogo, Malam Dogo!”
Halima kuwa ko wane karambani ya ja ta, da ganinsa sai ta
tsaya daga kofar zaurensu, ta ce, “Malam Dogo, Malam Dogo,
ka zo, baba na kira.”
Malam Dogo da ya ji haka sai ya nufo zauren. Halima ko ta
ruga zaure wajen ubanta, ta rungume shi tana kuka. Tsammaninta
wani dan sanho da wadan ke rataye a bayansa duk ba kome ciki
sai ‘yan yara kamarta. Malam Dogo ya zo, ya durkusa gaban
masassaki, ya ce, “Ga ni, ‘yar matan nan tawa ta ce kana kirana.”
Masassaki ya kawo sadakar abinci da goro da kwabo, ya ba
shi, ya ce, “Tun da Halima ta kira ka, ai lalle in sallame
ka.” Malam Dogo ya yi godiya, ya bude sanho ya fitad da wata
‘yar nakiya da aka ba shi sadaka, ya mika mata, ta ki karba,
don ita ce gamuwarsu ta fari.
Daga ran nan kullum kuma in zai wuce sai ya biyo ta zauren
gidan, in ya ga Halima a waje ya ba ta dan wani abin da ya
samo sadaka. Tun tana gudu, yau da gobe har ta saba da shi,
ta rika tsayawa tana karba.
Da ya gan ta dai saiya zauna, ta hau bias kafarsa suna wasa.
In ta fara irin ‘yan tambayoyin nan nata na yara, sai shi
kuma ya rika ba ta amsa irin yadda ya kamata. In ta tamyabe
shi, “Me ke cikin sanhonka?” Sai ya amsa mata, “Tuwo da nama
da sukar.” In ta ce, “Ina innarka?” Sai ya nuna ungulu ko
shirwa, ya ce, “Ga ta nan tana tashi.” Sai su bushe da dariya.
Duk sa’ad da yarinyan nan ta ga ungulu ko shirwa sai ta ce,
“A! Ga innar Malam Dogo.” Ta dubi uwarta, ta ce, “Inna, ke
ba ki iya tashi kamar innar Malam Dogo?” Uwar ba ta ko kulawa
da ita in ta fara tambayarta.
Suna nan haka, ashe wadan nan wani mai sihiri ne, ba a sani
ba. Ran nan sai ya zo wurin masassaki dauke da ‘yan kayansa
Halima ta tambaye ka inda na ke, ka ce ni ma na yi fiffike
na tashi kamar innata, don kada ta yi kuka. Kullum ku ce mata
zan dawo gobe.”
Masassaki ya yi bakin ciki, don ‘yarsa ta rasa abokin wasa.
Ya shiga gida ya dauko wata tsumman riga, ya ba Halima ya
ce ta kawo wa Malam Dogo a zaure. Yariyna ta jawo riga da
gudu, ta kawo masa. Ta fada jikinsa tana murna.
Malam Dogo ya dube ta, duk idonsa suka cika da hawaye domin
sabo. Ya zauna nan har margariba. Da suka yi salla, ya ci
abinci, sai ya kira masassaki, suka fita bayan gari, suka
yi tafiyar kamar loko guda cikin daji, sai suka kai ga wani
dutse. Da suka isa, wada ya dubi masassaki, ya ce, “Ka san
an ce soyayya gamon jinni ce, ko ba haka ba?”
Masassaki ya ce, “Hakannan ne.”
Wada ya ce, “To, tun da na zo garin nan, ban ga wanda jinina
ya hadu da shi kamar ‘yarka ba, Halima. Tun da tana tsorona,
har ka ga yanzu ba wanda ta ke so da gani irina. Kome ta ci
ta rage mini. Kai kuma kana yi mini alheri iyakar gwargwado.
Saboda haka ni kuma zan saka maka. Ko da ya ke kana ganina
haka a wulakance, don in jarrabi mutane shi ya sa na wulakanta
kaina. Nan kasar duk kafin ka sami wanda ya ke al’amari da
aljanu kamata, ka dada.” Ya tsuguna ya tara ‘yan hakukkuwa,
ya debi ganyayen kan dutse, ya yi turare.
Masassaki ya rike baki ya ga al’ajibi. Da hayaki ya tashi,
sai Malam Dogo ya dubi dutse, ya ce, “Fayau, bude dutsen kudi!”
Nan da nan sai dutse ya bude. Da budewarsa sai Malam Dogo
ya dauki wata ‘yar fitila nan rataye cikin dutsen, ya kunna.
Masassaki ya duba cikin kogon dutsen nan, ba abin da ke ciki
sai karfe ja wur cikin wata katuwar randa. Ya bude baki yana
mamaki.
Malam Dogo ya ce, “Na ba ka abin da ke cikin dutsen nan
duka, amma da sharadi guda. Duk sa’ad da ka zo, kada ka debi
abin da ya fi fam guda kowance zuaa. Na san fam guda dai ya
ishe ka kashewa yini guda. Daga nan har ka mutu ba ka ganin
kudin nan na raguwa. Ka lura in Halima ta isa aure ka yi mata
kaya masu kyau, ga dai gudummuwata nan na bayar.”
Masassaki ya fadi yana godiya, yana rokon Malam Dogo gafara
in ya yi masa wani laifi da. Suka gafarta wa juna. Malam Dogo
ya ce, “Ko da rana ka zo sai ka diba, in dai ba ka gudun kada
mutane su gan ka. In ko da dare za ka zo, in ka fita, ka yi
turare da ganyen nan, ka tabbata ba wani abin firgita da zai
dame ka. In ko ka zo, ka ga abin da na yi ba wani abu ba ne
mai wuya. Sai ka debi ganyen nan na bias dutse, ka yi turare
da shi a gidin dutsen, ka ce, ‘Fayau, bude dutsen kudi.’ In
ka shigo, ga fitila ka kunna, in da dare ka zo. In da rana
ne ko, ba ruwanka da ita. Ka kuma amince, ba kayan aljannu
ne ka ke sata ba, balle ma ka ce za ka ji tsoro. Kai dai ban
da dibar abin da ya fi fam guda kullum.”
Ya dubi masassaki ya ce, “Fara daga yau.” Masassaki ya duka
ya kidaya fam guda, suka fito. Malam Dogo ya ce, “Garam, kulle
dutsen kudi!” Dutse ya koma ya rufe.
Malam Dogo ya dubi masassaki ya ce, “To, sai mu yi ban kwana,
ni zan wuce.” Suka yi sallama. Malam Dogo ya wuce, masassaki
ya koma gida yana tsalle-tsalle don murna. Ya kwashe duk labari
ya gaya wa matar, amma bai gaya mata abin da za a ce da dutsen
ya bude ba. Suka yi ta murna.
Gari na wayewa, ko da magariba ta yi sai ya koma ya debo
fam guda. Ya I ta yin haka kullum. Nan da nan kafin wata takwas
ya sa aka debe dannin gidansa, aka gina masa na kasa. Aka
yi zauruka kamar goma sha biyu kafin a shiga gidan. Aka ta
da soraye. Ya kwashi kayan sassaka duk ya kona.
Cikin mako guda ya auri ‘yam mata uku, ya gama da matarsa,
suka yi hudu. Duniya ta komo sabuwa, sai katta ke ta kaiwa
suna komowa cikin gida. Aka manta da kiransa Maikujera, sai
aka lakaba masa Maigida. Da ya yi magana sai zabura a gama
abin da ya ce, kome ya fadi sai ka ji barori na cewa, “Allah
ya kyauta yin maigida.”
Bai cika shekara ba sai da ya daure doki goma sha biyu a
bargarsa suna harbin iska. Da ya hau sai a bi shi tii, kamar
Sarki. Mutane suka yi ta al’ajibin yadda ya yi arziki haka.
Suka ga ko ba ya saye ba ya sayarwa, amma kullum abin nasa
gaba gaba ya ke ci. Da mai garin da wadansu sun fara hassadar
abin, suna kushewa. Amma daga baya, da suka ga hassadarsu
ta zama taki, sai suka saki, suka mika kai neman abin sutura.
Da ba ya girman kai da wannan abu, amma daga bisani mutane
da makada da maroka suka kumbura shi, har ya fara hura hanci
da makada da maroka suka kumbura shi, har ya fara hura hanci
yana alfahari, tun ba in ya je dutsen kudi ya ga abin kamar
ba alamar karewa.
Ran nan yana zaune bias kujera, sai ya ce a ransa, “Kai,
ni fa wahalar zuwa dutsen kudin nan kullum ta dame ni. Kullum,
gemai-gemai da ni, a ga na nufi daji saboda fam guda. To,
ni ba abin in ki zuwa ba, don ina so in kwashe kudin duka
inda yana yiwuwa. Gobe dai fam biyu zan debo gaba daya in
gani. Watakila dai Malam Dogo ya ki barina ne, don kada in
huta wa raina. Amma fa ina amfanin a ga kamata ya tashi ya
shiga daji don fam guda?”
Ko da magariba ta yi, sai ya tafi dutsen kudi, ya debo fam
biyu, ya fito. Sai ya ce, “Haba, na san da ma abin nan na
Malam Dogo ya rufe ni ne. Tun da ya ke dai nawa ne, mene ne
na yi mini haka?”
Ya yi kamar wata guda yana diban fam biyu biyu kullum. Sai
wata rana ya ce, “Shin me ya sa ne zan rika wahala da kaina
don ‘yam fam biyu tak? An ce ba sata na ke yi ba. To, ba na
kawo abina diga, kowa ya huta, ni ma ko in sami hankalina
ya kwanta in yi kiba, da wannan wahalar shiga daji kullum,
sai ka ce talaka?”
Sai ya sami buhunan gishiri ya ajiye, ya ce, “Gobe da wadannan
za ni, in rika cika su ina kawowa gida har in kwashe sarai,
in huta da shan dari kullum magariba.”
Gari na wayewa, ko da magariba ta yi sai ya kwashi buhunan
ya nufi dutsen, yana takawa sai ka ce namijin agwagwa, don
cikin ‘yar shekaran nan guda da rabi ya zama sai ke ce taiki
don kiba. Ni’ima da cin dadi duk sun sa har furfurarsa ta
koma baka. Ya yi tsar, shuni ya huda shi, jikinsa sai kalli
ya ke yi.
Da ya isa sai ya zauna ya huta, yana kulla abin da zai yi
a ransa sake wani. Matansa kuma duk ya kamata ya sake su,
don tun da suka kai ga shekara guda da rabi a dakunansu ai
sun tsufa.
Da ya gama kulle-kullen abin da zai yi, ya tashi ya shiga
kogo da buhuna. Ya ajiye su gefe guda, ya dauki daya don ya
cika sa hannu zai diba, sai ya ga randar kudin ta yi kasa,
ta bace. Dutsen kuma ko kasa ko bias, sai aka bar Usuman jikan
Usuman nan tsugune yana sallallami, yana da na sani sa’ad
da ba ta da amfani. Ya kwashe ‘yam buhunansa, ya nufi gida
yana bakin ciki.
Da ma ai irin bukatarsa ka san ba tari ya ke yi ba. Kafin
wata uku dan abin hannunsa duk ya kare, ya sayad da dawakinsa,
barorinsa da suka ga abin na lalacewa suka watse. Da wadannan
kudi na dawaki suka kare, ya karyar wa mai garin da gidansa
araha, ya yi awo da kudin.
Kafin shekara wannan dan hatsin ya kare, sai matan nan yara
suka fita, suka bar shi da tsohuwar matarsa. Da ma an ce tsohon
doki sai mai shi.
In gajarce maka labari dai, na rantse har da rawaninka,
Allah ya be ka nasara, ba a yi shekara biyu ba, sai da ungulu
ta koma gidanta na tsamiya. Ka ji aikin zari. Kowa ya I kokarin
wai ya sami fiye da abin da Allah ya ba shi, ya lalace.
[insert picture here—middle right page 92]
Kafin aku ya kare ba da labarin nan gari ya wayer. Musa ya
dubi Barakai, ya ce, “Kin ga irin halin nasa ba?”
Barakai ya ce, “A’a! Ashe kana da gaskiya, ka ji abu kamar
na magani! Wallahi ko da ya fara labarin sai na ji na manta
abin da ya kawo ni. Amma ba kome na dawo da magariba.” Ya
fusata, ya ce, “har kai ma watau tatsuniyoyinsa sun rude ka
ko? To, gobe ka fito ba da shi ba, ka ga abin da zai same
ka.”
Da magariba ta yi sai ya Barakai ya yiwo shiri ya dawo,
ya ce wa Musa, “Zan sake kwana nan gunka, yau lalle mu fita.
Suka zauna suka yi ta hira. Da suka ji bayin nan sun yi shiru
suka iske aku, Musa ya ce, “Zan tafi, ga shi har na sami ‘yar
rakiya kuma.”
Aku ya duba ta taga sai ya ga hadari ya taso, ya ce wa Musa,
“Haba, ko kuna hauka kwa fita yanzu cikin wannan ruwa?”
Barakai ya ce, “Ai ba a fara ruwa ba, ma tafi hakannan.”
Aku ya yi ta jansu da ‘yan tade-tade, har ruwa ya goce. Suka
zauna suna jira a dauke.
Aku ya dube su, ya ce, “Da zaman banza bari in gaya maku
dan labari.”
Musa ya dubi Barakai, ya ce, “Ai ko kin san gaskiyarsa,
ya fada mana dan gajere.”
Barakai ya ce, “Kyale shi, ba mu so. Kullum sai ka rika
tsai da shi a kan surutun wofi, kai ba hadisi ka ke masa ba,
kai ba labaran Annabawa ka ke gaya masa ba, balle a san kara
shi ka ke yi.”
Aku ya ce, “Abin da ya sa ba na ba da labaran Annabawa,
tsoron jahilai na ke. Kun san yanzu akwai mutane da yawa wadanda
su ba malamai ba na sosai, amma da sun ji mutum ya yi wata
‘yar magana game da irin wadannan, sai ka ga suna neman daukar
kafarsa, wai ya yi sabo. Amma fa im ba don gudun haka su tabbata
a gare shi—har zuwa ga Shugaban Ma’aika, akwai wanda ba sani
ba?”
Musa ya ce, “To, in haka ne fara gaya mana labarin Annabi
Sulaimanu, wanda aka ce ya mallaki mutane da aljannu har da
tsuntsaye.”
Aku ya ce, “Wannan ai sananne ne har yanzu ba ka ji shi
ba?”
Musa ya ce, “I, na ji cikin dukan mutanen duniya babu wanda
ya fi shi arziki”
Aku ya ce, “Ai wannan daga baya ne. Domin sa’ad da aka nufe
shi da annabci aka ce ya zabi dukan abin da ya ke so a ba
shi. Shi ko ya ce tun da ya ke an ba shi mulkin jama’ar Allah,
shi ba abin da ya fi so sai hikima, don ya san yadda zai rike
su a kan adalci. To, tun da ya zabi wannan bai zabi dukiya
ba, ko tsawon rai, ko mutanen zamaninsa, ya kuma kara masa
har da abubuwan nan da bai roka ba.”
Musa ya ce, “Habe, tun da na ke ban taba samun wanda ya
bayyana mini asalin wannan a;’amari ba, sai fa kai yau.”
Aku ya ce, “Ko labarin yadda ya yi hukunci tsakinin wadansu
mata biyu ba ka taba ji ba?”
Musa ya ce, “Wallahi ban taba ji ba. Wane irin huknci ya
yi?” Aku ya matso kusa da Musa, ya kishingida a bias hannun
rigarsa, ya fara.
|
|