|
Wata rana Sarki yana kilisa, sai ya tarad da wani
dan kwikwiyo yana kwance, duk kiyashi sun cika bakinsa nishi
ya ke yi dai dai, kansa. Ko yaya aka yi ya rabu da uwarsa, Allah
kadai ya sani.
Da Sarki da dube shi sai tausayi ya kama shi, ya ja linzami
ya tsaya, ya dubi mutanen da ke biye da shi, ya ce, “A, kakkabe
wa Sarkin Babanni ya lura da shi da kyau yana ba shi abinci,
in yana da sauran kwana gaba ya tashi.”
Nan da nan, kafin Sarki ya rufe baki, bayi sun dira sun
kama karen, sun shafe masa baki da hannanyen rigunansu. Wani
ya sa shi kan kwacciya, ya tafi da shi gida ya kai wa Sarkin
Babanni, ya Sarki. Da rana ta yi sanyi suka komo.
Bayan kamar kwana uku sai dan kare ya farfade, har ya fara
tafiya, Da ya sami kamar wata biyu sai ya zama kamar ba shi
ba. Ya yi bulbul, duk inda Sarki za shi yana biye. Da ya girma
sai kullum dare in Sarki ya shiga barci, shi kuwa sai ya zo
kofar Saboda haka Sarki ya rika sonsa kwarai da gaske. Ba
mai ikon ya buge shi, ko ya yi masa wata katuwar tsawa, don
tsoron Sarki.
Ana nan, ran nan safiyar Salla Sarki ya yi shiri zai fito
ya hau zuwa idi, sai karen nan ya biyo. Sarki ya waiwaya ya
gan shi, ya buga masa tsawa, ya koma daki ya kwanta, don ya
san haka a kan yi masa in ba a son ya bi.
Yana nan kwance dakin Sarki, can an kusa saukowa daga idi,
sai aka kare toye-toyen Salla. Wata sadaka ta fara dauko kwano
guda ta kawo cikin dakin nan ta aijye. Amma maimakon ta rufe
abincin yadda ya kamata sai ta bar shi a bude, don ta san
ko da zai rube karen nan ba shi tabawa.
Karen nan yana kwance, sai ya ga wani kumurci ya biyo matakin
soro, ya sauko daga kan azara, ya sa baki cikin abincin yana
ci. Kare ya fita wage yana haushi don mutane su zo. Ba wanda
ya kula da shi.
Da mata suka ji ya dame su da hausahi, sai suka dauki dutse
suna jifarsa, don sun ga Sarki ba ya nan. Da karen nan ya
ga ba su gane abin da ya ke nufi ba, sai ka kyale ya shiga
daki ya kwanta. Maciji kuma da ya ga ya koshi, sai ya sulale
ya koma cikin azara abinsa ya shige.
Can an jima Sarki ya dawo. Da shigowarsa iyali suka yi masa
barka da sauka. Bayan sun tashi, ya nufi wajen abincin nan
zai ci. Kare ya bi shi yana kada wutsiya kamar ya ce, “Kada
ka ci, maciji ya zuba dafi a ciki.” Allah bai ba shi ikon
magana ba.
Sarki ya wanke hannu ya sa cikin abinci abinci, ya yanko.
Kare kuwa sai ya kai nan ya kai na, Sarki na tsammanin son
abinci ya ke yi. Ya jefa masa ya ki ci, sai haushi ya ke yi
wa Sarki.
Sarki ya bude baki zai sa wannan lomar sa’an nan ya dauki
sanda ya kore shi, sai karen ya yi farat ya buge hannun Sarki,
loma ta fadi kasa. Sarki ya dunkula hannu ya shiga dimar kare,
amma kare sai gurnani ya ke, bai kula ba. Ya sa baki ya cinye
loman nan da ta fadi daga hannun Sarki, ya kuma hau wa sauran
abincin duk ya cinye sarai. Tun Sarki na dukansa, har haushi
ya kama shi, ya gaji ya bari. Ya tsaya kurum ya ga ikon Allah.
Ko da kare ya cinye abincin nan, sai ya koma gefe guda ya
kwanta. Kafin Sarki ya kare ciccika, kare ya mimmike nan ya
mutu.
Ganin wanan abu fa ya kara ta da hankalin Sarki, ya ce,
“Lalle akwai wani abu game da abincin nan. Watakila sadakar
da ta kawo ta yi mini sammu ne in ci in mutu.”
Sai sarki ya fito ya kira ta, ya tambaye ta, tarantse da
abin da zai kasha ta ba ta sa kome ba ciki. Ya tantambayeta
ko ta bari garin sauran kishiyoyin, ta ce a’a, da karewa sai
ta zuba cikin wannan kwano ta kawo.
Sarki ya ce, “To, da kika fita ba wadda ta shigo bayanki?”
Sadaka ta ce, “Mts, bayana ba wadda ta shigo. Ba na daukan
akhakin wani, ni kadai na dawo na bude, don ya sha iska da
na ji kuna tafe.”
Sarki ya yi shiru, ya ce, “Lalle karya ku ke yi. Munafincinku
na mata wane ne bai san shi ba? Ba shakka ki gaya mini abin
da kuka zuba, in ba haka ba kuwa in sa a yanka ki.”
Sadaka ta fadi tana ahi, tana rantse-rantse tana cewa ba
ta sa kome ba ciki. Ya dube ta, ya ce, “Ke ar, munafuka!”
Ya aika a kira bayi su zo su yanka ta. Nan da nan suka shigo,
aka café ta tana kuka, aka yi waje da ita.
Sarki ya yi zugun cikin daki, yana mamakin abin da ya yi
wa sadakan nan har da ta ke so ta kasha shi, ya rasa. Can
sai ya ji sadakan nan har da ta ke so ta kasha shi, ya rasa.
Can sai ya ji dakin ya gume da wani wari kamar na gwano. Ya
tashi ya inda ya ke zaune, bai ga gwano ba. Yana kakkabe rigarsa
ko ya shiga ciki, sai ya ji ka-ka-ka-ka-ka a bias rufin daki.
Ko da ya daga kansa sai ya ga wani katon kumurci a cikin azara.
Da ya gan shi sai ya san lalle barin abincin nan da ta yi
a bude ne, macijin nan ya zo ya ci. Saboda haka ya tashi da
sauri, ya tafi inda bayin dandanne za su yanka, sai kuka ta
ke tana salati. Sai ya ce, “Kai, ku tsaya, ku tsaya!”
Bayi suka tsaya suna kaduwa, suna tsammani Sarki ya raina
saurinsu ne. Sarki ya ce, a sake ta. Ya kira bayin, ya tafi
da su turakarsa, ya nuna musu kumurcin. Ya gaya musu kuma
da abin kumurcin kasa, aka fid da shi wage aka yar.
Sarki ya tara dukan iyalinsa, ya gaya musu wannan al’amari,
ya kuma gargade su kada su sake barinabinci a bude. Nan gabansu
kuma ya gafartra wa sadakan nan, suka koma sha’aninsu.
Ya sa aka fita da Karen nan zaure, ya gaya wa fadawa da
Sarakunansa abin da ya auku cikin gida duka. Ya sa aka gina
dan daki a kofar gidansa, aka yi wa karen nan kabari a ciki
aka sa shi. Ya yi bakin ciki kwarai saboda mutuwar Karen nan.
Ya kuma gargadi mutanensa da abu biyu. Na daya, ya ce kada
su rika saurin fushi, kowane a’amari ya auku, kafin su zartad
da hukunci su tsaya sai sun bi cikin al’amari ya auku, kafin
su zartad da nan sun yi saurin cika umurin da ya bayar a yanka
sadakan nan da ya yi da na sani daga baya. Na biyu, ya ce
su kyautata tausayi da jin kai ga dabbobi da tsuntsaye, ko
da ba su da dabara kamaru, ba a san inda rana za ta fadi ba.
Kowa ku ka gani a duniya, yana da ranarsa. Ko ba don wannan,
ma ba, ai an ce aikata alheri ga kowa, sakayyarka tana wurin
Allah.
Da Waziri ya ji haka sai ya ce a rana, “A’a! Me ya ke nufi
da wannan labari? Dan tsuntsun nan fa rigima gare shi! Yana
tsammani ni yaro ne, balle ya ce ya yi mini wa’azi?” Sai ya
hadiye fushinsa, ya yi murmushi, ya ce, “Wannan labari naka
iyaka ne. Bari in yi maka kyauta.” Sai ya zaro wani zobe na
zinariya ya rike a hannun hagu,ya nufo aku wai zai ba shi,
hannunsa na dama ko na cikin riga. Aku ya rika tsalle yana
ja da baya, Waziri na binsa yana cewa, “Tsaya mana ka karba!”
Aku na ja da baya dai yana cewa, “Ai sadaka na yi maka labarin,
ban don ka biya ba.”
Da Waziri ya lura aku ya gane shi, sai ya zabura gaba daya
ya kai masa bugu, aku ya goce, buje ya tadiye Waziri ya fadi,
ya daushe baki har hakorinsa guda ya fita. Ya tashi ja wur
cikin jinni, nan da nan baki ya haye.
Da aku ya ga haka sai ya haye cediyar kofar gidan, ya kaikaici
idon Waziri ya yi ta dariya. Da ya ga Waziri da dubo, sai
ya kanne, ya ce, “Sannu bawan Allah! Ba ka sani ba, Waziri,
ni kuwa ban ji zafin ba. Da ka taba jin labarin yautai da
wani mai keke, da ba ka kulla wannan niyya ba game da ni.
Kana so in kare ka da shi?”
Wzairi dai bai ce uffan ba, yana can yana fama da abin da
ya same shi. Aku ya faki idonsa ya yi masa gwalo, ya ce, “Ko
ba ka so ina gaya maka, aimu abimmu muna yi don Allah ne.
Sai ya soma.
|
|