Hausa Hausa English
Wakokin Hausa

Chat Room
Check your mai

Classified Ad

Jaridu


Mahada

 

 

 

 

Alhaji Mamman shata
 


  Alhaji Dr. Mamman shata Katsina a halin da ake ciki yanzu ya zamewa makada da mawakan Hausa Dutse baka daukuwa saida gammo, mutsu-mutsu gobe jar kasa, ruwan dare mai gama duniya, ya buga da mazajen farko gashi yana bugawa da mazajen yanzu. Abinda marokinsa ke fada ke nan kafin ya fara wakarsa ta Bakandamiya. Babu wata kasa a duniya da zata bugi kirji ita kadai tace ta sami ci gaba a rana guda. Su kansu kasashen da suka ci gaba irin su Amirka, Tarayyar Soviet, China, Birtaniya da Japan da Jamus sun yi amfani ne da kyawawan al'adunsu wajen gina tushen ci gaban da suka samu. Mawaka da makadan wadannan kasashe da suka ci gaba sun bada gudummawa mai yawan gaske ta fuskar irin tasu fasahar wajen ciyar da kasashen nasu gaba.

Farfesa Dandatti Abdulkadir, kafin ya zama shugabanjami'ar Bayero dake Kano a Nijeriya, ya rubuta makalarsa ne kan rayuwa da wakokin Alhaji Mamman shata sannan ya gabatar wa shaihunan Malaman Amirka don su tabbatar masa da samun digirinsa na uku (Ph. D). Wannan yunkuri na Abdulkadir Dandatti ya tabbatar da cewa shaharar da Alhaji Mamman Shata yayi, ba a Nijeriya kawai ta tsaya ba harma da wadansu manyan kasashen duniya.

Cikakken sunan Shata shine Muhammadu. Sunan Mamman lakani ne irin wanda kakanni kan radawa jikokinsu tun suna yara. Ita kuwa kalmar "Shata". lakani ne wanda ake kiransa da shi lokacin da yak-e cinikin goro. Baba Magaji Salamu Musawa, wanda a lokacin shine ubangidan Alhaji Mamman shata, shi ya rada masa sunan "Shata". A lokacin da Alhaji Mamman shata ke saida goro, ba'a san wata aba wai ita bakar goro ba, goron kawai ake sayarwa hamsin-hamsin, kuma a kan saida guda-guda. Cinikin baka na kasa goro ana sayarwa da guda-guda ai sai kananan 'yan goro, inji Alhaji Mamman shata. A wancan lokacin da Alhaji Mamman shata ke saida goro baya kirgawa, sai dai ya kwasa ya baiwa mai saye dai-dai kudinsa, shi yasa ake ce masa -shata- wato mai saida goro babu kidayawa sai ya shata ya bayar. Kalmar shata nada wata ma'ana daban kamar ace a shata fill, amma wadda ake amfani da ita wajen sunan Alhaji mamman shata ita ce ta diban abu a bayar kamar ba'a so.

Kafin zuwan turawa kasar Hausa, al'ummar Hausawa na da addininsu na Musulunci, akwai kuma kadan dake bin addinin gargajiya da ake kiransu Maguzawa. Ba'a san hikimar rubuta sunayen yara da shekarunsu a ajiye don tarihi ba kamar yadda yanzu ake yi. Wannan shi yasa ba'a san cikakkiyar shekarar da za'a ce an haifi Alhaji Mamman shata ba.Amma a shekarar da ya kai ziyara gidan rediyon Amirka cikin 1989, yace shekarunsa 65 a wancan lokaci, an kuma yi hassashen cewar an haife shi cikin 1926.

 



{talla}

Littatafan Hausa

 
Gidajen Rediyo Hausa

 

 

       
 

Mohammed Hashim Gumel ya tsara ya gina wannan shafi. Kofar mu a bude take bisa duk wasu shawarwari da kuma ra'ayoyinku, kan wannan fili, da kuma irin abinda kuke so mu rika wallafawa."Gyara kayanka bai zama sauke muraba ba." Ana iya aiko mana da wasika ta layi kamar haka mhashim@gumel.com

@Gumel.com 1998 Wannan fili an kareshi da dokar wallafawa, a nemi izzini kafin amfani da kayan mu.